Tarihin Ahlul Baiti A


Na biyu: Sun yarda da Sahabbai



Yüklə 296,5 Kb.
səhifə3/3
tarix17.09.2018
ölçüsü296,5 Kb.
#68718
1   2   3

Na biyu: Sun yarda da Sahabbai

An karvo daga Abu Hazim yace, wani mutum yazo wurin Ali binul Hussaini sai yace, me nene matsayin Abubakar da Umar a wurin Manzon Allah (SAW)? Ali binul Hussaini yace masa, irin matsayinsu a yanzu. Ya nuna qaburburansu. Ya na nufin yadda su ke a kwance yanzu kusa da juna haka kusancinsu ya ke a lokacin rayuwarsu, haka kuma ya ke a aljanna.85

Daga Ja'afar binu Muhammad daga babansa yace, wani mutum yazo wurin babana, yana nufin Zainul Abidin Ali binul Hussaini, yace, Ba ni labarin Abubakar. Sai yace, Siddiq ka ke nufi? Sai mutumin yace masa, kai ma ka na kiransa haka? Sai yace, kai ar! Ba ka waxanda su kayi masa wannan suna ba? Waxanda su kayi masa wannan suna ai sun fi ni. Manzon Allah ne (SAW) da Muhajirai da Ansarai. Wanda ko duk bai kira shi "Siddiq" mai cikakkiyar gaskatawa ba, to kada Allah ya gaskata maganarsa. Ni ina ba ka shawarar kaje ka so Abubakar da Umar, ka qaunace su, in hakan laifi ne na xauke maka.86

Muhammad binu Haxib yace, wasu mutane sunzo ma Ali binul Hussaini daga Iraqi, sai suka rinqa aukawa a cikin mutuncin Abubakar da Umar da Usman (R.A). To, a lokacin da suka qare kalamansu sai Imam yace da su: Ku ba ni labari su wane ne ku? Shin ku ne Muhajirai na farko da Allah Ya ce:



﴿ لِلْفُقَرَاءِ الْمُهَاجِرِينَ الَّذِينَ أُخْرِجُوا مِنْ دِيارِهِمْ وَأَمْوَالِهِمْ يَبْتَغُونَ فَضْلًا مِنَ اللَّهِ وَرِضْوَانًا وَيَنْصُرُونَ اللَّهَ وَرَسُولَهُ أُولَئِكَ هُمُ الصَّادِقُونَ (8)

Ma'ana:

(Ku yi mamaki) ga matalauta masu hijira waxanda aka fitar daga gidajensu da dukiyoyinsu, suna neman falala daga Allah da kuma yarda, kuma suna taimakon Allah da manzonSa! Waxannan su ne masu gaskiya.

Suratul Hashri, Aya ta 8.

Sai su ka ce, A`a. Ya ce: to, ku ne:



﴿وَالَّذِينَ تَبَوَّءُوا الدَّارَ وَالْإِيمَانَ مِنْ قَبْلِهِمْ يُحِبُّونَ مَنْ هَاجَرَ إِلَيْهِمْ وَلَا يَجِدُونَ فِي صُدُورِهِمْ حَاجَةً مِمَّا أُوتُوا وَيُؤْثِرُونَ عَلَى أَنْفُسِهِمْ وَلَوْ كَانَ بِهِمْ خَصَاصَةٌ وَمَنْ يُوقَ شُحَّ نَفْسِهِ فَأُولَئِكَ هُمُ الْمُفْلِحُونَ (9)

Ma'ana:

Da waxanda suka zaunar da gidajensu (ga musulunci) kuma (suka zavi) imani, a gabanin zuwansu, suna son wanda ya yi hijira zuwa gare su, kuma ba su tunanin wata buqata a cikin qirazansu daga abin da aka bai wa muhajirai, kuma suna fifita waxansu a kan kawunansu, kuma ko da suna da wata larura. Kuma wanda aka kiyaye shi daga rowar ransa to, waxannan su ne marabauta.

Suratul Hashri, Aya ta 9.

Sai su ka ce, A`a. Ya ce: To, ga shi ku kun sheda ba ku cikin waxannan biyun. Ni kuma na shaida ba ku cikin na ukkun su ne:

﴿وَالَّذِينَ جَاءُوا مِنْ بَعْدِهِمْ يَقُولُونَ رَبَّنَا اغْفِرْ لَنَا وَلِإِخْوَانِنَا الَّذِينَ سَبَقُونَا بِالْإِيمَانِ وَلَا تَجْعَلْ فِي قُلُوبِنَا غِلًّا لِلَّذِينَ آَمَنُوا رَبَّنَا إِنَّكَ رَءُوفٌ رَحِيمٌ (10)﴾
Ma'ana:

Kuma waxanda suka zo bayansu, suna cewa, "Ya Ubangijinmu! Ka yi gafara a gare mu, kuma ga 'yan uwanmu, waxanda suka riga mu yin imani, kada Ka sanya wani qulli a cikin zukatanmu ga waxanda suka yi imani. Ya Ubangijinmu! Lalle Kai ne Mai tausayi, Mai jinqai. Suratul Hashri, Aya ta 10.


Sa`annan ya ce da su: Ku fita ku bani wuri. Allah Yayi mu ku kaza da kaza (ma`ana yayi addu`a maras kyau akansu).87

A wata ruwaya kuma cewa yayyi, Ku tashi ku ba ni wuri! Kada Allah ya kusanta gidajenku domin ku ku na lavawa ne ga musulunci don kuyi varna, amma ku ba musulmi ba ne.88

Akwai mamaki ga waxannan mutane da irin qarfin halinsu wajen sukar Sahabban Manzon Allah (SAW), da yadda ta qoqarin rusa musulunci.

Wa nene ya kawo ma na Alqur'ani?

Wa nene ya cirato mana rayuwar Manzon Allah (SAW) da ayyukansa?

Wa nene ya xauko musuluncin kacokan bayan ya yi jihadi wajen kariyarsa, ya kutsa birni da qauye ya na yaqi, don ya isar da shi zuwa ga remu?

Su wa nene Allah yace, ya yarda da su kuma sun yarda da shi?

Duk waxannan ba su ne Sahabban Manzon Allah (SAW) ba? Ba sune surukansa ba? Sun yi tarayya kuma da shi a wasu jikoki.89

Duk mai sukar su to, addinin ne yake suka. Wanda ya soke su ba sauran Alqur'ani a gurinsa don ba shi da hanyar saninsa.

Wanda ya tuhumce su da sun canza wani abu a cikin littafin Allah kuwa, to, littafin Allah xin ya qaryata shi.

Wanda yace sun canza bayan Manzon Allah (SAW) sun yi ridda bai yarda da abin da Allah yace ba kenan cewa, ya yarda da su. Domin kuwa ya za'a yi wanda Allah ya yarda da shi ya bar shi ya vace har ya kai ga ridda?

FASALI NA TAKWAS

Wafatinsa

An karvo daga Abu Ja'afar cewa, lokacin da mutuwa tazo ma mahaifinsa Ali binul Hussaini ya yi kuka. Sai nace masa baba me ya sa ka kuka alhalin kuwa ni ban tava ganin wanda ya bautata ma Allah kamarka ba?

Sai yace, Ya xana! Idan Alqiyama ta yi ba sauran mai iko. Kowa ya na a qarqashin ikon Allah har Annabawa da Mala'iku. Wanda Allah yaso sai ya kai shi aljanna, wanda yaso kuwa sai a yi wuta da shi.90

Ali binul Hussaini ya rasu a shekara ta 95 B.H. kamar yadda Malam Yahya binu Kasir yace.91

Amma wasu masana sunce, a shekara ta 94 B.H. ya rasu, ya na da shekaru 58 a duniya. Wasu masanan kuwa na da ra'ayin cewa, tun a shekarar 92 ko 93 B.H. ne Allah ya karvi ransa.92

Bayan yi masa sallah an kai shi a maqabartar baqi'ah in da aka yi jana'izarsa.

Anan ne za ka ga qarshe na gaskiya ga wannan rayuwa. Allah mabuwayi yace,
إِنَّكَ مَيِّتٌ وَإِنَّهُمْ مَيِّتُونَ سورة الزمر: 30

Ma'ana:

Lalle ne kai (Manzon Allah) mai mutuwa ne, Kuma lalle ne su ma masu mutuwa ne.

Suratuz Zumar, aya ta 30
وَمَا جَعَلْنَا لِبَشَرٍ مِنْ قَبْلِكَ الْخُلْدَ أَفَإِنْ مِتَّ فَهُمُ الْخَالِدُونَ سورة الأنبياء : 34

Ma'ana:

Ba mu sanya ma wani mutum tabbata ba a gabaninka. To, idan ka mutu su za su dawwama ne?

Suratul Anbiya' aya ta 34

Wannan ita ce rayuwar xan adam. Kome tsawon ranka watarana zaka mutu. Ko wane ne abokinka watarana zaka rabu da shi.

Kaji daxi yadda ka ke so, amma fa tabbas sai ka rabu da shi. Mutuwa kenan! Mai wargaza jin daxi, mai kore farin ciki. Wasu lokuttan mu tuna, a wani yanayin kuma sai mu shimga.

Ali binul Hussaini bai yi kuskure ba da yace a cikin wani waqensa;

Mu kan firgice idan mutuwa ta juyo

Mu na koma wasarmu idan mun ka mance

Misalin namu wanda ya hangi zaki

Idan ya ba da bai ko sai ya mance93



Kammalawa

Ya xan uwa!

Ga mu dai tare da kai mun kammala wannan saqo, bayan mun yawata a cikin tarihin wannan bawan Allah wanda xaya ne daga fitattun 'yan gidan annabta, kuma wanda 'yan sha biyun shi'a ke gadara da jingina kansu zuwa ga reshi.

Daga abin da ya gabata dai ka na iya fahimtar wane ne Zainul Abidin bisa gaskiyar Allah babu za'ida. Mu na iya taqaita darussan wannan xan littafi kamar haka;


Darasi Na xaya

Tataccen tauhidi shi ne aqidar da Ahlulbaiti su ka rayu akansa. Ba su kiran kira kowa don neman biyan buqatunsu sai mahaliccinmu. Ba su kiran Annabi ko Mala'ika ko Waliyyi ko wani zavavve, domin sanin da su kayi cewa, wannan haqqen Allah ne shi kaxai. Ba mai amfanar kansa da kome a duniya sai da yardar Allah ballantan ya amfani wani. Wanda ko Allah ya nufi shi da samun cuta ba mai kuranye ta daga kunsa sai shi Allah mahalicci.

Ga abin da Allah yace ma mushrikai da su ka nemin agajin wani ba shi ba;
إِنَّ الَّذِينَ تَدْعُونَ مِنْ دُونِ اللَّهِ عِبَادٌ أَمْثَالُكُمْ فَادْعُوهُمْ فَلْيَسْتَجِيبُوا لَكُمْ إِنْ كُنْتُمْ صَادِقِينَ سورة الأعراف: 194

Ma'ana:

Lalle ne duk waxanda ku ke kira koma bayan Allah su bayi ne irinku. To, sai ku kira su, su kuma su karva maku in har kun kasance masu gaskiya (a kiran da ku ke ma su). Suratul A'raf, aya ta 194


Darasi Na biyu;

Kyakkyawar alqar da ke tsakanin Sahabbai da Ahlulbaiti, iyalan gidan Manzon Allah (SAW). Wannan hujja ne akan soyayyar gakiya da qaunar da su ke ma junansu.

Sau tari ne Ahlulbaiti su ka kare martabar almajiran mai gidansu, su na yaba ma su, su na mayar da martani akan mai sukarsu, su na jaddada kira ga qaunarsu da jivintarsu. Wannan kuwa ba zai asali ba da kyakkyawan yabon da Allah ya yi ma su (Sahabban) a cikin tsarkakakken littafinsa, kamar in da ya ke cewa;
لَقَدْ تَابَ اللَّهُ عَلَى النَّبِيِّ وَالْمُهَاجِرِينَ وَالْأَنْصَارِ الَّذِينَ اتَّبَعُوهُ فِي سَاعَةِ الْعُسْرَةِ مِنْ بَعْدِ مَا كَادَ يَزِيغُ قُلُوبُ فَرِيقٍ مِنْهُمْ ثُمَّ تَابَ عَلَيْهِمْ إِنَّهُ بِهِمْ رَءُوفٌ رَحِيمٌ سورة التوبة: 117

Ma'ana:
Darasi na Uku:

Irin kyawawan xabi'un wannan bawan Allah kamar son jama'a da kyautata ma su, da haquri akan cutawarsu, da nisantar abin hannunsu duk su na daga cikin xabi'un annabta da ya gada daga iyaye da kakanninsa.


Darasi na Huxu;

Cikakken tsoron Allah shi ne wanda ya ya ke gadar da yin aiki da tsare ibada. Zainul Abidin kuwa ya dace da wannan suna nasa a wannan fage.


Darasi na biyar;

Qarya ne ace Ahlus Sunnah su na gaba da Ahlulbaiti a da ko a yanzu, domin kuwa babu wanda ya san haqqensu bisa ga adalci kamar Ahlus Sunnah. Mu tuna irin yabon da limaman Sunnah su ka yiwa wannan bawan Allah. Haka su ke da duk sauran ire irensa daga zuri'ar Annabi mai tsarki.


Daga qarshe, Ina 'yan uwana masu qaunar iyalan Manzo, masu jin daxin jingina kansu zuwa ga resu? A daina faxin maganar fatar baki wadda ba ta kai zucci. A koma ma rayuwar waxannan bayin Allah ayi koyi da su a maganganunsu da ayyukansu. Masoyi fa shi ne mai koyi da masoyinsa.

Wannan kiran na fara shi da kaina sannan da sauran 'yan uwana musulmi na ko wace xariqa da ko wace mazhaba. Muzo muyi aiki da kalamai da ayyukan Ahlulbaiti don mu haxa kanmu wuri xaya kamar yadda su ka kasance a tasu rayuwa, wataqila zamu samu haske da zai kai mu wurin Allah mu same shi a cikin yarda da mu ba cikin hushi ba.

Ya Allah! Ga yi gafar ga remu da 'yan uwanmu musulmi da su ka riga mu bada gaskiya, Kada ka sanya damuwa a cikin zukatanmu a game da waxanda su ka yi imani. Lalle ne ya Ubangijinmu Kai ne Mai tausyi, Mai jinqai.

Allah ya yi tsira akan annabinmu Muhammad da iyalansa da Sahabbansa baki xaya.94


Manazarta

Al Bidayah Wan Nihayah, na Ibnu Kathir Ad Dimashqi, Bugun Farko, Dar Ar Rayyan Lit Turath.

Tarikh Madinati Dimashq, na Hafizh Ibnu Assakir As Shafi'i, Dar Al Fikr.

Tahdhib Al Kamal, na Hafizh Ibnu Hajar Al Asqalani, Bugun Farko, Muassasatur Risalah.

Tahdhib At Tahdhib, na Hafizh Ibnu Hajar Al Asqalani, Bugun Farko, Dar Al Ma'rifah.

Al Jami' As Sahih, na Imam Abu Isa At Tirmidhi, Bugun Farko, DAr Ihya' At Turath.

Hilyatul Auliya' Wa Xabaqatul Asfiya', na Hafizh Abu Nu'aim Al Asfahani, Bugun Farko, Dar Al Kutub Al Ilmiyyah.

Dam'atun Ala hubbin Nabiyy, na Abdullahi binu Saleh Al Khudairi, An buga shi a jerin littafan Al Muntadal Islami, Huququn Nabiyy bainal ijlali Wal Ikhlal, Bugun Farko.

Siyar A'lam An Nubala', na Imam Shamsud Din Muhammad binu Ahmad Addhahabi, Bugu na Sha xaya, Muassasatur Risalah.

Sahih Al Bukhari, na Imam Muhammad binu Isma'il Al Bukhari, Dar Al Qalam, Beirut.

Sahih Muslim, na Imam Muslim binul Hajjaj, Dar Ihya' At Turath Al Arabi.

Sifatus Safwah, na Imam Ibnul Jauzi, Bugun Farko, Dar Al Fikr.

Ax Xabaqat Al Kubra, na Imam Ibnu Sa'ad Al Basri, Bugu na biyu, Dar Al Kutub Al Ilmiyyah.

Musnad Al Imam Ahmad, na Imam Ahmad binu Hambal, Dar Al MA'arif.

Littafan Shi'ah:



Bihar Al Anwar, bugun Al Wafa, Beirut, 1403H.

Sharh Ihqaq Al Haqq, na Al Mura'shali, Maktabatu Ayatillil Uzhmah Al Mura'shali, Qum, Iran, 1415H.

Kashful Gummah, na Arbili, Bugun Al Adwa', Beirut.

1 Masana sun qari juna sani game da Ahlulbaiti iyalan gidan Manzon Allah (SAW). Magana mafi rinjaye ita ce cewa, Ahlulbaiti su ne waxanda aka haramta masu cin sadaqa daga Banu Hashim da Banul Muxxalib saboda dangantakarsu da Manzon Allah (SAW). Duba: Nailul Auxar, na Imam As Shaukani, a Babin dalilin fassara iyalan Manzon Allah waxanda ake sanyawa ga salati (2/77), da kuma Jala'ul Afham, na Shehun Malami Ibnul Qayyim, Shafi na 109.

2 Za ka iya samun cikakken tarihin Sahabbai a waxannan littafai; Al Isabah fi tamyizis Sahabah, na Ibnu Hajar Al Asqalani, da Usdul Gabah fi Ma'rifatis Sahabah, na Ibnul Asir, da kuma Al Isti'ab fi Ma'rifatil Ashab, na Ibnu Abdil Barri Al Qurxubi.

3 Waxannan kuma tarihinsu ya na a cikin Siyar A'lam An Nubala' na Imam Dhahabi, da Hilyatul Auliya', na Abu Nu'aim, da Al Xabaqat Al Kubra, na Ibnu Sa'ad da sauransu.

4 Duba gabatarwar da aka yi a bugu na biyu na littafin Risalatul Mustarshidin, na Haris Al Muhasibi, tahaqiqin Ustaz Abdul Fattah Abu Guddah, Shafi na 12.

5 Duba littafin da ya gabata, kuma a wannan shafin.

6 Wani baitin waqe ne da yazo a cikin littafin Saidul Khaxir, na Ibnul Jauzi, Shafi na 448.

7 Duba Sahihul Bukhari, a Kitabus Salati, Babin masallatan da ke akan hanyoyin MAdina, Hadisi na 461.

8 A nan ya na da kyau mu lura cewa, Ibnu Umar ya na neman albarkacin aiki ne ba albarkacin wuri ba. Koyi da Manzon Allah (SAW) anan shi ne manufa ba wuraren ba. Duba labarin a cikin Siyar A'lam An Nubala' (3/213).

9 Duba littafin Al Manhaj Al Ahmad fi tarajumi Ashabi Ahmad (1/93).

10 Duba littafin da ya gabata.

11 Duba gabatarwar Sahihu Muslim, Shafi na 78.

12 Al Muhaddisul Fasil, Shafi na 6

13 Ikhtiyaru Ma'rifatir Rijal, na Xusi (1/324) da Biharul Anwar, (2/217) da Mustadrak Al Wasa'il, na Xabarsi (9/90).

14 Tirmidhi ne ya fitar da shi a littafinsa, daga hadisin Anas, Hadisi na 2423, a cikin Kitabu Sifatil Qiyama, da kuma Ibnu Majah a nasa littafin, Hadisi na 4241, a littafin Zuhdu, Babin tuba.

15 Aqidatu Ahlilbaiti, na Abdullahi Al Khudair, Shafi na 27, daga Rijal Al Kasshi, Shafi na 225-226.

16 Jami' Bayan Al Ilim Wa Fadlihi, (2/32).

17 Imam Ahmad ne ya ruwaito shi daga Hadisin Ubadah binu Samit, Hadisi na 21693 a cikin Musnadul Ansar.

18 Al Bagwi ya kawo shi a Sharhus Sunnah, (13/43).

19 Tahzib Al Tahzib, (1/148).

20 Duba cikakken labarin a Tafsirin Ibnu Jarir Al Xabari (10/119).

21 Wannan qa'idar Ibnu Rajab ya faxe ta. Duba: Qawa'id fit ta'amuli ma'al Ulama, Shafi na 133.

22 Jami'u Bayanil Ilmi Wa Fadlihi (2/48).

23 Muslim ya fito da shi, Hadisi na 4425, a Fada'il Ali, Ahmad ma ya ruwaito shi, Hadisi na 18464 a farkon Musnadin Kufawa daga Zaid binu Arqam, kuma Darimi ya fitar da shi, Hadisi na 3182, a Fada'il Al Qur'an.

24 Tirmidhi ya ruwaito shi, Hadisi na 3722, a darajojin Ahlu Baitin Nabiyyi. Tirmidhi xin kuma yace, ya na da kyau, amma yana da xan rauni.

25 Bukhari ya ruwaito shi, a Babin darajojin dangin MAnzon Allah (SAW) daga Kitabu Fada'il As Sahabah, Hadisi na 3439.

26 Bukhari ya ruwaito shi a Babin darajojin dangin Manzon Allah (SAW) daga Kitabu Fada'il As Sahabah, Hadisi na 3435. Kuma Muslim ya ruwaito shi, Hadisi na 3304, Babin faxar Annabi (SAW) cewa, ba a gadonmu. Kuma Ahmad ya fitar da shi, Hadisi na 52, a Musnadin Abubakar As Siddiq.

27 Dam'atu Ala Hubbin Nabiyy, littafin da aka buga a jerin Kitabul Muntada Al Islami, Huququn Nabiyyi (SAW) bainal Ijlali wal Ikhlal, Shafi na 50.

28 Al Islam bainal Ulama'i Wal Hukkam, na Abdul Aziz Al Badri, Shafi na 159, daga Al Madarik, na Alqali Iyal, Shafi na 293.

29 Dam'atu Ala Hubbin Nabiyy, littafin da aka buga a jerin Kitabul Muntada Al Islami, Huququn Nabiyyi (SAW) bainal Ijlali wal Ikhlal, Shafi na 50.

30 Baitocin waqar Di'ibil Al Khuza'i guda bakwai da mai littafi ya kawo ya na da matuqar wuya a fassara su kai tsaye zuwa harshen hausa musamman in ba ga gwanayen harshen ba kuma wataqila mawaqa. Abin da na faxa dai shi ne ma'anarsu. Mai karatu ya karvi uzurina. Daga Mai Fassara. Duba cikakkiyar waqar a littafin da ya gabata, Shafi na 50.

31 Al Xabaqatul Kubra, (5/165) da Hilyatul auliya' (3/161), da Tahdhibul Kamal, (5/138), da Tarikh Madinati Dimashq, (41/374), da Al Irshad na Mufid (2/141) da kuma Kashful Gummah, na Arbili (2/297).

32 Idan kana son qarin haske game da haqqoqan Ahlulbaiti na Shari'ah ka duba littafin Alul Bait Wa Huququhum As Shar'iyyah, na xan uwana Sheikh Saleh Ad Darwish.

33 Ummu walada ita ce kuyanga wadda aka ganimance ta a wurin jihadi da zaran ta haifu ta samu wani yanki na 'yanci wanda ke hana a sayar da ita. Shi ya sa ake kiranta Ummu walada.

34 Sifatus Safwah, (2/54) da Siyar A'lam An Nubala' (4/386).

35 Wafayat Al A'yan Wa Anba' Abna' Az Zaman, (2/127).

36 Duba littafin: Al Imam Zainul Abidin Qudwatus Salihin, na Ayatullahi Muhammad As Shirazi, da Al Imam As Sajjad qudwatun wa Uswah, na Muhammad Taqi Al Madrasi.

37 Shi ma Sayyiduna Ali ya ribanci kuyangarsa Al Hanafiyyah ne a yaqoqan ridda da Sayyiduna Abubakar ya yi. Ita ce kuma ta haifa ma sa Muhammad Al Asgar wanda aka fi sani da Ibnul Hanafiyyah.

38 Tahdhib Al Tahdhib (4/185) da Tarikh Madinati Dimashq, (41/361).

39 Siyar A'lam An Nubala' (4/386).Su ma dai littafan Shi'ah sun yi savani akai. Duba littafin Shirazi da na Madrasi misali.

40 Sifatus Safwah, (2/54) da Siyar A'lam An Nubala', (4/386) da Ax Xabaqat Al Kubra, (5/163).

41 AL Biadayah Wan Nihayah, (5/173) da Sifatus Safwah, (1/344).

42 Al Xabaqat Al Kubra, (5/163).

43 Tarikh Madinati Dimashq, (41/374) da Siyar a'lam An Nubala', (4/390) amma fa Dhahabi yace, isnadin maganar ya yanke.

44 Siyar A'lam An Nubala', (4/389).

45 Al Bidayah Wan Nihayah, (5/109) da Sifatus Safwah, (2/57) da Siyar A'lam An Nubala', (4/387).

46 Al Xabaqat Al Kubra, (5/164) da Tarikh Madinati Dimashq, (41/370).

47 Al Bidayah Wan Nihayah, (5/114) da Sifatus Safwah, (2l57) da Siyar A'lam An Nubala' (4/398).

48 Al Bidayah Wan Nihayah, (5/110).

49 Siyar A'lam An Nubala', (4/398).

50 Sifatus Safwah, (2/58) da Siyar A'lam An Nubala' (4/392) da Tahdhib Al Kamal, (5/239).

51 Tadhkiratul Huffazh, (1/75).

52 Sifatus Safwah, (2/55).

53 Tarikh Madinati Dimashq, (41/382)

54 Littafin da ya gabata, (41/380).

55 Sifatus Safwah, (2/54) da Siyar A'lam An Nubala', (4'391) da Tahdhibul Kamal, (5/238).

56 Hilyatul Auliya', (3/157) da Siyar A'lam An Nubala', (4'392) da Ax Xabaqat Al Kubra, (5/167) da Tarikh Madinati Dimashq, (41/378).

57 Tahdhibut Tahdhib, (4/185).

58 Sifatus Safwah, (2/56) da Siyar A'lam An Nubala', (4'393) da Hilyatul Auliya', (3/160) da Tarikh Madinati Dimashq, (41/383).

59 Siyar A'lam An Nubala', (4'393) da Ax Xabaqatul Kubrah, (5/196) da Hilyatul Auliya', (3/165) da Tarikh Madinati Dimashq, (41/388).

60 Al Bidayah Wan Nihayah, (5/120).

61 Sifats Safwah, (2/55).

62 Sifatus SAfwah, (2/55) da Ax Xabaqatul Kubra, (5/172) da Tarikh Madinati Dimashq, (41/384).

63 Siyar A'lam An Nubala', (4'394).

64 Siyar A'lam An Nubala', (4'393) da Hilyatul Auliya', (3/160) da Sifatus Safwah, (2/56).

65 Sifatus Safwah, (2/56).

66 Sifatus Safwah, (2/58) da Siyar A'lam An Nubala', (4'394) da Tahdhibul Kamal, (5/239).

67 Siyar A'lam An Nubala', (4'388) da Hilyatul Auliya', (3/162) da Tarikh Madinati Dimashq, (41/369) da Sharh Ihqaq Al Haqq, na Sayyid Al Mura'shali, (28/453).

68 Tahdhibul Kamal, (5/238) da Tarikh Madinati Dimashq, (41/376).

69 Siyar A'lam An Nubala', (4'387).

70 Sifatus Safwah, (2/54).

71 Siyar A'lam An Nubala', (4'398) da Musnad Ar Rida, na dawud Al Gazhi, Shafi na 160, da Sharh Ihqaq Al Haqq,na Sayyid Al Mura'shali, (28/105)

72 Siyar A'lam An Nubala', (4'388) da Hilyatul Auliya', (3l162) da Tarikh Madinati Dimashq, (41/369) da Al Irshad na Mufid (2/143) da Biahrul Anwar, (46/74).

73 Tahdhibul Kamal, (5/240).

74 Duba littafin da ya gabata.

75 Sifatus Safwah, (2/75) da Al Bidayah Wan Nihayah (5/113).

76 Sifatus Safwah, (2/55).

77 Tarikh Madinati Dimashq, (41/387).

78 Wanda ya yi wannan waqar a larabce shi ne, Mahmud Al Warraq, wanda ya rasu a shekara ta 225 B.H. Ka duba littafin Al Mustaxraf fi Kulli Fannin Mustazraf, shafi na 205.

79 Hilyatul Auliya' (3/162) da Tahdhibul Kamal, (5/239) da Tarikh Madinati Dimashq, (41/386).

80 Yana nufin kuxin garawa. Duba Siyar A'lam An Nubala', (4/391) da Tahdhibul Kamal, (5/238) da Tarikh Madinati Dimashq, (41/377).

81 Tahdhibul Kamal, (5/240) da Jiahdul Imam As Sajjad, na Muhammad Rida Al Jalali, Shafi na 109.

82 Ax Xabaqatul Kubra, (5/163).

83 Bukhari ya fitar da shi a Kitabul Adhan, Babin idan Liman bai cika Sallah ba amma Mamu ya cika.

84 Abu Dawud ya ruwaito shi a Kitabus Salati, Babin limancin na gari da mugu.

85 Siyar A'lam An Nubala', (4/395) da Tahdhibut Tahdhib, (4/185) da Tahdhibut Tahdhib, (5/239).

86 Siyar A'lam An Nubala', (4/395) da Tahdhibul Kamal, (5/239) da Tarikh Madinati Dimashq, (41/388) da Jihadul Imam As Sajjad, Shafi na 103.

87 Sifatus Safwah, (1/56) da Hilyatul Auliya' (3/161).

88 Al Bidayah Wan Nihayah, (5/112) da Tahdhibul Kamal, (5/239) da Al Fusul Al Muhimmah, na Ibnus Sabbag (2/864) da Kashful Gummah, na Arbili, (2/291).

89 Misali Ja'afar Al Sadiq, mahaifiyarsa ita ce, Ummu Farwa Bintul Qasim bin Muhammad bin Abibakar. Don haka, Sayyiduna Abubakar shi ne kakan Al Sadiq da Al Kazim da Al Hadi da Ar Rida da Al Jawad duk daga cikin Ahlulbaiti.

90 Tarikh Madinati Dimashq, (41/379).

91 Siyar A'lam An Nubala', (4/400).

92 Al Bidayah Wan Nihayah, (5/119).

93 Tarikh Madinati Dimashq, (41/410).

94 An gama wallafa wannan littafi da hantsin ranar Arafah a shekarar 1426 B.H Kuma ni ne bawa mabuqaci zuwa ga Allah, Abdu Aziz binu Ahmad bin Abdillaxif Al Umair. Mai fassara kuma ya kammala a yau daren assabar 20 ga Shawwal 1427 B.H. a Kaduna. Allah ya sa mu yi tarayyar lada a wannan aiki, ya sa mu samu ceton Manzonsa don qaunarmu ga iyalansa.


Yüklə 296,5 Kb.

Dostları ilə paylaş:
1   2   3




Verilənlər bazası müəlliflik hüququ ilə müdafiə olunur ©genderi.org 2024
rəhbərliyinə müraciət

    Ana səhifə